Mutane 7 cikin masallatan da aka kona sun rasu

Date:

Daga Nura Adam Lajawa

 

Rohotannin da ke Isa ke jaridar kadaura24 na tabbatar da cewa akalla mutane 7 sun rasu daga cikin mutane kusan 30 da aka Cinnawa wuta a garin larabar abasawa dake karamar hukumar Gezawa a Kano.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito wani matashi ya banka wuta kan wasu masallata a garin larabar abasawa yayin da suke tsaka da sallar asuba ta wannan rana ta laraba.

Iftila’i: Ana fargabar sama da mutane 30 sun kone suna tsaka da sallar asuba a wani masallaci a Kano

Wakilin kadaura24 da a yanzu haka yake garin ya tabbatar mana cewa tuni an yi jana’izar mutane biyu da suka fara rasuwa cikin mutanen da suka konen.

Matashin da ya bankawa masallata wuta a Kano ya bayyanawa yan sanda dalilinsa na yin aika-aikar

Yanzu haka kuma mutane biyar sun kara mutuwa wadanda aka dakon kai kawawwakin su daga asibitin Murtala zuwa garin domin yi musu sutura kamar yadda Addinin Musulunci ya yi tanadi.

Tuni dai yan sanda suka tabbatar da kama wanda ake zargi da cinna wutar, Inda ya fada musu cewa yayi hakan ne saboda kokarin da yan uwansa ke yi na hana shi gadonsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...