Da dumi-dumi: Jami’an EFCC sun kai samame kasuwar WAPA ta Kano

Date:

Daga Aliyu Abdullahi Fagge

 

Rahotanni da muke samu yanzu na nuna cewa jami’an hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC sun kai samame kasuwar Chanjin kudaden waje ta WAPA dake Kano .

Wani Dan Kasuwar da kadaura24 ta zanta da shi Bisa sharadin sakaye sunansa, yace jami’an hukumar ta EFCC a yau litinin sun kai samame har sau uku a wannan rana.

Hasashen yanayin da zai kasance yau Litinin a birnin Kano da wasu jihohin Nigeria

” Da fari kafin a Fara hada-hada sosai a kasuwar da misalin karfe 12 na rana sai ga jami’an hukumar ta EFCC chan wajen karfe 2 kuma suka sake dawowa, awa daya bayan tafiyar su kuma sai suka sake dawowa cikin kasuwar, hakan yasa duk muka gudu”. A cewar sa

Yan sanda a Kano na bincike kan mutuwar jami’in kwastam da ake zargin ya kashe kansa

Ana dai ganin samamen da jami’an hukumar ta EFCC sun kai kasuwar ta Wapa yana da nasaba da yadda a yan Kwanakin nan Dala ke cigaba da hauhawa.

Kuma har lokacin hada wannan rahotan jami’an hukumar ta EFCC suna cikin kasuwar ta Wapa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...