Rundunar Yan Sandan ta Bayyana Matsayarta Kan Harsashin Da ya Taba Dan Jarida a Gidan Gwamnatin Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce a halin yanzu tana gudanar da bincike kan lamarin wani harsashi da ya taba wani dan jarida mai aiki a gidan gwamnatin Kano.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Usaini Gumel, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Najeriya hakan a wata tattaunawa ta wayar tarho a Kano ranar Asabar, inda ya ce rundunar na kan bincike kan lamarin .

Harbin Bindiga: Wani Dan Jarida ya Tsallake Rijiya da Baya a Gidan Gwamnatin Kano

Ya ce duk shugabannin hukumomin tsaro da ke sanya ido kan harkokin tsaro a gidan sun tsaya kai da fata akan lamarin, wanda hakan yasa aka bincika makaman jami’an tsaro da ke bakin aiki a lokacin da lamarin ya faru, kuma duk an tabbatar alburusansu suna nan babu gibi.

Gwamnatin Kano ta Magantu Kan Harbin Da Aka Yiwa Wani Dan Jarida a Gidan Gwamnatin jihar

Ya bayyana cewa harsashin da akai harbin da shi, daga wajen gidan gwamnatin jihar kano aka harbo shi kuma suna bincke don gano daga inda aka harbo shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...