Mun dauki matakan shawo kan matsalar mai a Nigeria – NNPC

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL, ya ce ya shawo kan matsalar da ta jawo dogayen layuka a gidajen mai da ke faɗin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin yau Alhamis, NNPCL ya ce an samu matsalar ne saboda “ɗawainiyar wajen jigilar man”.

“NNPCL na tabbatar da cewa wahalar da ake sha wajen samun man fetur a wasu sassan Najeriya ta faru ne saboda matsalar da aka samu wajen jigilar man kuma yanzu an kawo ƙarshen ta,” in ji sanarwar.

Sanarwa ta Musamman Daga Hukumar Samar da Ruwan sha ta Jihar Kano

Kamfanin ya ƙara da cewa ba shi da niyyar sauya farashin man, wanda tuni ‘yan kasuwa suka ƙara farashinsa a jihohi.

Lita ɗaya ta man ta zarta N750 a Abuja babban birnin ƙasar.

Tun daga farkon makon nan aka fara ganin layuka a gidajen mai a Abuja, inda matsalar ta bazu zuwa jihohi daga baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...