Iftila’i: An Sami Gawar Wani Jariri Cikin Rijiya a Kano

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Wani abin takaici ya faru a Kano yayin da aka sami gawar wani jariri ya nutse a cikin rijiya da ke Ruguzau a karamar hukumar Takai a jihar.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Alhaji Saminu Abdullahi ya fitar a ranar Laraba.

Ya ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata.

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Bayyana Dalilanta na Rufe Bankin UBA A Jihar

Mun sami kiran gaggawa da misalin karfe 02:14 na rana daga wani Sabo Ladan cewa an tsinci gawar wani jariri a cikin wata rijiya a garin ruguzau.

“Nan take muka aika da tawagar mu zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 02:18 na rana. Da isa su wajen sai suka sami jariri a cikin rijiyar,” inji shi.

A cewarsa, an fito da jaririn daga rijiyar a sume kuma daga baya aka tabbatar da cewa ya mutu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...