Yan sanda sun gurfanar da mutum 104 a kotu kan zargin ayyukan daba a Kano

Date:

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta gurfanar da mutum 104 da ake zargi ƴan daba ne a gaban wasu kotuna da ke unguwar Nomandsland.

An kama mutanen a wuraren hawan sallah da masarautun Kano ke yi duk shekara a bukukuwan sallah.

Wata Bakuwar Cuta Ta Yi Ajalin Mutane 45 A Kano

Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan a shafinsa na Fesbuk inda ya ce ana zargin mutanen da laifukan daba da riƙe makamai da kuma ta’amali da miyagun ƙwayoyi.

Kotu ta tabbatar da dakatar da Ganduje daga APC

Kiyawa ya ce an samu kama mutanen ne bayan binciken da aka yi a sashen binciken manyan laifuka na rundunar kamar yadda kwamishinan ƴan sandan jihar, CP Mohammed Usaini Gumel ya umarta.

A baya-bayan nan ma rundunar ƴan sandan ta Kano ta kama wasu da ta ce ƴan daba ne waɗanda kuma suke addabar unguwar Ɗorayi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...