Kotu ta tabbatar da dakatar da Ganduje daga APC

Date:

Babbar kotu a jihar Kano ta tabbatar da dakatarwar da aka yiwa shugaban jam’iyyar APC na ƙasa Abdullahi Umar Ganduje daga jam’iyyar.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito wasu shugabannin APC na mazabar Ganduje dake karamar hukumar Dawakin Tofa sun ce sun dakatar da Shugaban jam’iyyar APC na kasa Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

Zargin almundahana: Ganduje da iyalansa basu halarci zaman kotun ba

Umarnin dakatarwar ya fito daga Mai sha’ira Usman Malam Na’abba, kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Kotun ta umarci da Ganduje kada ya kuma kiran kanshi a matsayin shugaban jam’iyyar ta APC, sannan kar ya sake shiga ko jagorantar duk wani al’amari na jam’iyyar APC.

Tinubu na son in ci gaba da zama shugaban APC – Ganduje

Dr. Ibrahim Sa’ad ne ya shigar da karar a madadin wasu daga cikin shugabannin APC na mazabar Ganduje da suka hadar da mataimakin sakatare na mazabar Lamin Sani da Halilu Gwanjo mai bada shawara kan harkokin shari’a a gaban kotun mai shari’ar Usman Malam Na’Abba.

Kotun ta umarci wadanda ake kara da cewa kowa ya tsaya a matsayinsa har zuwa ranar da za’a saurari karar a ranar 30 ga watan afirilu 2024.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...