Zargin almundahana: Ganduje da iyalansa basu halarci zaman kotun ba

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Tsohon gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje da iyalansa basu halarci zaman kotun, da aka gudanar ba a wannan rana bisa tuhumarsu da laifin almundahana na biliyoyin naira.

Rashin bayyanar Ganduje a gaban kotun a yau ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin wadanda suke je sauraren karar, yayin da suke kokarin tantance ko rashin bayyanar Ganduje Rashin girmama kotu ne .

Tinubu na son in ci gaba da zama shugaban APC – Ganduje

Sauran wadanda ba su halarci kotun ba sun hada da matarsa, Farfesa Hafsat Ganduje, danta, Umar Ganduje, da wasu mutane 5 da ake zargi .

Sai dai ba a bayyana dalilin da ya sa tsohon gwamnan wanda kuma shi ne shugaban jam’iyya mai mulki na kasa ya kasa bayyana a gaban kotu, amma wasu makusancinsa da ba a bayyana sunansa ba ya bayyana cewa “Dr. Ganduje ba ya kasar.”

El-Rufa’i Ya Fara Kalubalantar Gwamnatin Tinubu

A ranar 9 ga Afrilu, 2023 babbar kotun jihar Kano ta bayar da sammaci ga shugaban jam’iyyar APC na kasa da ya gurfana a gaban kotu a ranar 17 ga watan Afrilu kan zargin almundahana na biliyoyin naira da aka tafka a lokacin da yake kan mulki.

Har zuwa lokacin hada wannan rahotan, ba a bayyana ko ya aike da wakilci kotun ko a’a ba .

Majiyar jaridar kadaura24 ta independent Post ta rawaito ana sa ran kotun za ta bayar da cikakken martani kan rashin halartar duk wanda ake tuhuma.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...