Halin da Ake Ciki Game da Neman Watan Sallah Karama a Saudiyya

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Rahotanni daga Kasar Saudiyya na nuni da cewa tuni hukumar kula da duban wata ta Kasar ta fita tare da ba baza jami’an ta domin fara duban watan a wannan rana ta litinin.

Yanzu-yanzu: CBN Ya Sake Karya Farashin Dala a Nigeria

KADAURA24 ta ruwaito Jami’an sun girke kayan aikin wadanda da suka haɗar da na’urori na zamani domin su gudanar da aikin na su yadda ya kamata.

 

Sai dai masana ilimin taurari a Kasar sun cewa zai yi yuwa a ga jinjirin watan na Shawwal na shekara ta 1445.

Majalisar Dokokin Edo Ta Tsige Mataimakin Gwamnan Jihar

Hakan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da shafin Haramain na internet ya fitar a wannan rana.

“Galibin masana ilmin taurari sun yarda cewa zai yi wahala a iya ganin jaririn watan Shawwal 1445 a yau, amma a cikin ‘yan kwanakin nan Sudair Observatory ta tabbatar da cewa sun yi kuskure a lokuta da dama”.

Sai dai wannan bayanin bai dakatar da jami’an duban watan daga aikin su na cigaba da neman jinjirin watan na Shawwal ba.

 

Sai dai rahotannin da suke iske mu yanzu haka da misalin karfe 3 saura a gogon kasar, yanayin hadari da gajimare ake fuskanta a yankin Riyadh da Tumair da Sudair dake kasar ta Saudiyya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr....

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...