Kungiyar Sanatocin Arewa ta nada sabon shugaba tare da cire kawu Sumaila daga mukaminsa

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

An nada Sanata Abdulaziz Yar’Adua a matsayin sabon shugaban kungiyar Sanatocin Arewa.

Sanatan dake wakiltar Katsina ta tsakiya kani ne marigayi shugaban ƙasar Nigeria Umaru Yar’adua .

Nadin nasa ya biyo bayan murabus din Abdul Ningi, Sanata mai wakiltar Bauchi ta tsakiya.

Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Karin Hasken Kan Umarnin Bude Bodar Nigeria da Nijar

Majalisar dattijai ce dai ta dakatar da Ningi na tsawon watanni uku saboda furucin da ya yi kan zarge-zargen a kasafin kudin 2024.

Matar Shugaba Tinubu ta bayyana dalilin da suka sa bata tsoron mutuwa

Ningi, a wata wasika da ya aike wa kungiyar, ya rubuta cewa, “Ina so in ajiye mukamina na shugaban kungiyar Sanatocin Arewa. Tabbas hakan ya zama dole saboda abubuwan da ke faruwa a Majalisar Dokoki ta Kasa da Arewa da ma kasa baki daya.”

 

Haka kuma, kungiyar ta bayyana Sanata Tahir Mungono mai wakiltar Borno ta Arewa a matsayin mai magana da yawunta da zai maye gurbin Sanata Sumaila Kawu wanda majalisar ta gargadi shi da ya daina raba mukamai da za su iya haifar da tarzoma a kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Magance sheye-shaye ne kadai zai kawo karshen matsalar tsaro da talauci a Nugeria – Shugabar LESPADA

Daga Usman Usman   Ambassador Maryam Hassan shugabar kungiyar wayar da...

‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers Ta Mayar Da Martani Kan Sauke Alhaji Usman Daga Mukamin Wazirin Gaya

Daga Isa Ahmad Getso ‎ ‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers ta bayyana...

Rahoto: An kwantar da Buhari a ICU a Landan

  Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin...

Kacibus: A karon farko an hadu tsakanin Gwamnan Abba da Sarki Aminu Ado a Madina

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   A karon farko an hadu tsakanin...