Bidiyon Dala: Kotu ta Yanke Hukunci Kan Karar da Ganduje Ya Kai Hukumar Yaki da Cin Hanci ta Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta yanke hukuncin cewa hukumar karbar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano ba ta da hurumin gudanar da bincike kan zargin karbar cin hanci da akewa tsohon gwamna Abdullahi Ganduje a wani bidiyon.

Majiyar kadaura24 ta Solacebase ta ruwaito cewa alkalin kotun, Mai shari’a Abdullahi Muhammad Liman a ranar Talata ya yanke hukuncin cewa laifin yana karkashin dokar tarayya da hukumar jihar ba ta da iko a kai.

Gwamna Abba Kabir Ya Mikawa Majalisar Kano Sunayen Kwamishinonin Da Zai Nada

Idan dai za a iya tunawa, Abdullahi Ganduje, tsohon gwamnan jihar Kano ya maka hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano a gaban kotu inda ya bukaci alkalai da su dakatar da binciken bidiyon dala da hukumar ta ce zata yi masa.

Sai dai Lauyan wanda ake kara na farko a karar, Hukumar Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano Barr. Usman Umar Fari ya ce za su daukaka kara kan hukuncin kotun.

Karin Bayani na nan tafe

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...