Kungiyar Sanatocin Arewa Zata Tura Tawaga Kasar Nijar

Date:

 

Ƙungiyar sanatocin jihohin Arewacin Najeriya ta ce za ta tura wakilanta jamhuriyyar Nijar, domin ganawa da shugabannin mulkin sojin ƙasar, kan yadda za a mayar da mulki ga farar hula.

Ƙungiyar ta ɗauki wannan matakin ne, bayan sanar da janye takunkuman da ƙungiyar ECOWAS ta ƙaƙabawa Nijar da Mali da kuma Burkina Faso waɗanda sojoji ke jan ragamar mulkin su.

Kungiyar Kwadago ta bayyana matakin da zata dauka idan aka kaiwa ya’yanta hari yayin zanga-zanga

Kakakin ƙungiyar sanatocin, Sanata Sulaiman Abdurrahman Kawu Sumaila ya ce ƙungiyar zata tura tawagar ba tare da ɓata lokaci ba.

Zargin Juyin Mulki: Helkwatar tsaron Nigeria ta Magantu ta Batu

Janye takunkuman da ECOWAS ta yi zai sake buɗe harkokin cinikayya da zai taimaka wajen warware matsalar ƙarancin abinci da magunguna da sauƙaƙa al’amura ga ƙasashen na Najeriya da Nijar da ke makwabtaka da juna.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da wata ƙungiyar malaman mususlunci ta Najeriyar ta yi kira da sojoji a Nijar da Mali da Burkina Faso da su koma cikin ƙungiyar ta ECOWAS.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...