Kungiyar Sanatocin Arewa Zata Tura Tawaga Kasar Nijar

Date:

 

Ƙungiyar sanatocin jihohin Arewacin Najeriya ta ce za ta tura wakilanta jamhuriyyar Nijar, domin ganawa da shugabannin mulkin sojin ƙasar, kan yadda za a mayar da mulki ga farar hula.

Ƙungiyar ta ɗauki wannan matakin ne, bayan sanar da janye takunkuman da ƙungiyar ECOWAS ta ƙaƙabawa Nijar da Mali da kuma Burkina Faso waɗanda sojoji ke jan ragamar mulkin su.

Kungiyar Kwadago ta bayyana matakin da zata dauka idan aka kaiwa ya’yanta hari yayin zanga-zanga

Kakakin ƙungiyar sanatocin, Sanata Sulaiman Abdurrahman Kawu Sumaila ya ce ƙungiyar zata tura tawagar ba tare da ɓata lokaci ba.

Zargin Juyin Mulki: Helkwatar tsaron Nigeria ta Magantu ta Batu

Janye takunkuman da ECOWAS ta yi zai sake buɗe harkokin cinikayya da zai taimaka wajen warware matsalar ƙarancin abinci da magunguna da sauƙaƙa al’amura ga ƙasashen na Najeriya da Nijar da ke makwabtaka da juna.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da wata ƙungiyar malaman mususlunci ta Najeriyar ta yi kira da sojoji a Nijar da Mali da Burkina Faso da su koma cikin ƙungiyar ta ECOWAS.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...