Gwamnatin Tarayya ta sake Bude Kantin Sahad Stores

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Hukumar da ke Kare Muradan Masu Saye ta Najeriya FCCPC ta sake buɗe katafaren kantin kayar da kayayyaki na Sahad Stores, bayan rufe shi.

A ranar Juma’a 16 ga watan Fabrairu ne hukumar ta garƙame babban kantin, saboda zargin yadda ake cuwa-cuwar sanya farashin kayayyaki a kantin.

Iftila’i: Goodluck Jonathan ya Mika Kokon Bararsa ga Yan Nigeria

Hukumar ta yi zargin cewa masu gudanar da katafaren kantin na ƙara wa abokan hulɗarsu kuɗin kaya fiye da farashin da ke maƙale a jikin kayan.

FCCPC ta ce hakan na tilasta wa kwantomomi biyan kuɗaɗe masu tsada don sayen kayayyaki.

To sai dai cikin wata sanarwa da mai riƙon muƙamin mataimakin shugaban hukumar, Adamu Abdullahi, ya fitar ya ce an sake buɗe kantin domin ci gaba da cinikayya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Inganta tsaro: Shugaban K/H Tarauni ya ba da fili domin gina ofishin Civil Defence a karkasara

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Shugaban karamar hukumar Tarauni, Alhaji Ahmed...

Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nada Malam...

Gwamnatin Kano ta bada hutun sabuwar shekarar Musulunci

Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana gobe Alhamis, 26 ga...

Ni da kaina na je ofishin EFCC – Ajiya

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon Babban Jami’in Kudi (CFO) na...