Gwamnatin Tarayya ta sake Bude Kantin Sahad Stores

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Hukumar da ke Kare Muradan Masu Saye ta Najeriya FCCPC ta sake buΙ—e katafaren kantin kayar da kayayyaki na Sahad Stores, bayan rufe shi.

A ranar Juma’a 16 ga watan Fabrairu ne hukumar ta garΖ™ame babban kantin, saboda zargin yadda ake cuwa-cuwar sanya farashin kayayyaki a kantin.

Iftila’i: Goodluck Jonathan ya Mika Kokon Bararsa ga Yan Nigeria

Hukumar ta yi zargin cewa masu gudanar da katafaren kantin na Ζ™ara wa abokan hulΙ—arsu kuΙ—in kaya fiye da farashin da ke maΖ™ale a jikin kayan.

FCCPC ta ce hakan na tilasta wa kwantomomi biyan kuΙ—aΙ—e masu tsada don sayen kayayyaki.

To sai dai cikin wata sanarwa da mai riΖ™on muΖ™amin mataimakin shugaban hukumar, Adamu Abdullahi, ya fitar ya ce an sake buΙ—e kantin domin ci gaba da cinikayya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related