Tsadar Rayuwa: Kungiyar Kwadago zata gudanar da zanga-zanga a fadin Nigeria

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Shugaban kungiyar kwadago ta Najeriya, Kwamared Joe Ajaero ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta mutunta yarjejeniyar da ta kulla da kungiyar kwadago kafin cikar wa’adin kwanaki 14 don kaucewa zanga-zanga a fadin kasar.

Kwamared Joe Ajaero ya bayyana haka ne bayan taron majalisar zartarwar kungiyar ta kasa ranar Juma’a a Abuja.

Kwamared Joe Ajearo ya ce NEC ta amince da fara zanga-zangar matukar ba a biya bukatun kungiyar kwadagon ba.

Da dumi-dumi: Hukumar Hisbah ta sake kama wata yar TIKTOK a Kano

Shugaban kungiyar Kwadagon ya jaddada cewa zasu gudanar da zanga-zanga a duk fadin Nigeria a ranakun 27 da 28 ga wannan wata sakamakon tsadar rayuwa da yan Nigeria suke fuskanta.

Matsalar tsaro: Malam Shekarau ya baiwa Tinubu Shawara

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito Karamin Ministan Kwadago da Aiki, Dr Nkieruka Onyejeocha ya tabbatar wa kungiyar kwadagon cewa gwamnatin tarayya za ta cika yarjejeniyar da aka cimma da Organised Labour.

Akalla an kulla yarjejeniya kusan guda 16 tsakanin gwamnatin tarayya da Kungiyar Kwadago ta NLC da TUC tun a watannin baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar kula da almajirai ta Kasa ta kaddamar da yiwa almajirai Rijista a Kano

Daga Saminu Ibrahim Magashi   Hukumar kula da almajirai da yaran...

Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban ƙasa – Barau Jibrin

Daga Isa Ahmad Getso Mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata...

Inganta tsaro: Shugaban K/H Tarauni ya ba da fili domin gina ofishin Civil Defence a karkasara

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Shugaban karamar hukumar Tarauni, Alhaji Ahmed...

Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nada Malam...