Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Gwamnatin Najeriya ta ce za ta ci gaba da biyan tallafin N35,000 da ta fara biyan ma’aikata domin rage radadin illar cire tallafin man fetur ga ma’aikatan ƙasar.
Gwamnatin ta kuma roki kungiyar kwadagon kasar da su janye yajin aikin da suka shirya yi na kwanaki 14.
Gwamnan Kano ya bada wa’adi da sharadi domin sauke wasu kwamishinoni
Karamar ministar Kwadago ta Najeriya, Nkeiruka Onyejeocha ce ta bada wannan tabbacin a Abuja a wajen wani taro da shugabannin ƙungiyoyin kwadagon biyu da aka yi kan wa’adin da suka bai wa gwamnati na tafiya yajin aiki idan ba ta cika musu bukatunsu ba a cikin makonni biyu.
An dai cimma yarjejeniyar ne ranar 2 ga Oktoba, 2023 mai dauke da abubuwa 16 da suka hada da ƙarancin albashin ma’aikata da tallafin naira 35,000 ga ma’aikata duk wata da dai sauransu.
Kotu a Kano ta Aike da Murja Kunya Gidan Yari
Onyejeocha ta kuma ce gwamnati ta kara kaimi wajen ganin an kammala aiwatar da wannan yarjejeniya.
Ministar ta kira taron ne domin bayyana wa ƙungiyoyin kwadagon yadda ake aiwatar da yarjejeniyar, da kuma jaddada aniyar gwamnati kan yarjejeniyar.
“Gaskiya ne da cewa mun kulla yarjejeniya, amma gwamnati ta nuna gaskiya kan wannan batu, kuma bisa la’akari da gaggawar lamarin ne na kira wannan taro domin tattaunawa ita ce hanya mafi dacewa a kodayaushe, kuma dukkan mu muna neman lafiya kasancewar mutanenmu.”
Ta yi nuni da cewa, yayin da martanin kungiyoyin kwadagon kan gazawar gwamnati na cika yarjejeniyar bai dace ba, yana da kyau ayi la’akari da cewa wasu abubuwa da ke cikin yarjejeniyar ba za a iya cim musu ba a lokaci guda.
Rahotanni sun ce an tashi daga taron ba tare da cimma wata matsaya ba dangane da bukatun.