Daga Halima Musa Sabaru
Gwamnan jihar Kano Abba Kabir, a ranar Talata ya gabatar da kudirin sauke kwamishinonin da ba su yi aiki ba a majalisarsa.
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito tun lokacin da gwamnan ya rantsar da kwamishinonin ta watan Yuni, 2023, ya umarci kwamishinonin da su mayar da hankali wajen aikin su idan kuma ba haka zai tsige duk wanda aka samu Bai tabuka komai ba.
Kotu a Kano ta Aike da Murja Kunya Gidan Yari
Don haka gwamnan ya umurci sakataren gwamnatin jiha (SSG) da ya bayar da fom tantancewa ga kwamishinonin domin su cike, kuma da shi ne za’a yi amfani wajen gano kokarinsu ko akasin hakan .
Gwamnatin Tarayya Tace ta Gano Hanyoyin Magance Hauhawar Farashin Abinchi a Nigeria
Gwamnan ya baiyan hakan ne yayin taron Majalisar zartarwa ta jihar taro 12, Wanda ya gudana a gidan gwamnatin jihar Kano.
Gwamna Abba Kabir Yusuf yace zai dauki matakin tsige duk wanda aka samu bai tabuka komai a Ofishinsa ba, tare kuma da maye gurbinsa da wani.
Gwamnan yace ana bukatar kowanne kwamishina ya mayar da fom din da aka bashi nan da Kwanaki 10.