Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman
Allah ya yiwa Jaruma a Cikin Shirin dadin kowa na tashar Arewa24 Fatima Sa’id wacce aka fi sani da Bintu rasuwa a wannan rana ta lahadi.
Ƴan uwan jarumar ne suka tabbatar wa Manema labarai rasuwar ta ta bayan fama da jinya.
Shugabannin Kananan hukumomi 3 a Kano sun fice daga APC zuwa NNPP
Tuni dai aka yi jana’izarta a unguwar Gunduwawa da ke Kano, kuma abokan sana’arta na ci gaba da jimamin rashinta.
Bayan Shirin Dadin Kowa Jarumar ta taka rawa a wasu Fina-Finan masana’antar kannywood da dama.