Yajin Aiki: Gwamnatin Tarayya ta Magantu Kan yunkurin Kungiyar Kwadago

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Gwamnatin Najeriya ta ce ba abu ne mai yiwuwa ba a zartar da wasu daga cikin bukatun kungiyar kwadago da aka cimma a watan Oktoban 2023, da gaggawa ba.

Karamar ministar kwadagon kasar, Nkeiruka Onyejeocha ce ta shaida wa ‘yan jaridu a yau Juma’a yayin amsa tambayoyi ga ‘yan jaridun.

Tinubu Ya Bayar da Sabon Umarni ga Yan Nigeria

Gwamnatin ta tarayya ta kara da cewa daya daga cikin yarjeniyoyin wadda take neman a samar da cibiyoyin sauya motoci zuwa masu amfani da iskar gas zai dauki lokaci kafin cibiyoyin su wadata ko’ina kuma kwamitin da ke kula da samar da cibiyoyin yana aiki tukuru.

A watan Oktoban bara ne dai bangarorin biyu suka cimma jerin yarjejeniyoyi da suka kunshi ragewa ‘yan kasar radadin talauci sakamakon cire tallafin man fetur da gwamnati ta yi.

Kungiyar Masu Makarantu Masu Zaman ta Janye Karar da Take Gwamnatin Kano Kotu

Sauran bukatun sun hada da samar da mafita ga darajar naira da tashin farashi da kuma matsalar tsaro da dai sauransu.

Kungiyar kwadago dai ta bai wa gwamnati wa’adin mako biyu da ta zartar da yarjeniyoyin ko ta tsunduma yajin aikin sai baba ta gani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...