Tinubu Ya Bayar da Sabon Umarni ga Yan Nigeria

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya wajabta karanta alkawarin biyayya ga Najeriya ( National Pleged) a duk tarukan gwamnati da na jama’a a kasar.

Kakakin shugaban kasar Ajuri Ngelale ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa ranar Alhamis inda ya ce yin hakan nuna girmamawa ne ga kasa da kuma karfafa biyayya ga dokokin kasa tare da alkinta al’adu da martaba kasa.

Dawo da Sanusi Matsayin Sarkin Kano Ba Zai Haifawa Kano Da Mai Ido Ba – Wata Kungiya ga Majalisa

Shugaban ya jaddada bukatar yin biyayya ga manufofin kasa da nuna kima ga dokokin kasa.

Da dumi-dumi: Kungiyar Kwadago ta Bayyana Ranar Fara Yajin Aiki a Nigeria

Taken na yi wa Najeriya alkawarin biyayya wanda Tinubu ya ce a yi bayan rera taken kasa, na neman yan kasa su zama masu gaskiya da biyayya ga kasarsu.

Umarnin ya zo ne daidai lokacin da Najeriya ke fama da rikice-rikice da tashin hankali tsakanin arewaci da kudancin kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...