Kungiyar Masu Makarantu Masu Zaman ta Janye Karar da Ta Kai Gwamnatin Kano Kotu

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Gamayyar kungiyoyin masu makarantu masu zaman kansu a jahar kano sun bayyana janye karar da suka shigar da gwamantin jihar kan ayyukan hukumar makarantu masu zaman kansu .

shugaban gamayyyar kungiyoyin masu makarantun a jihar kano Injiyana Bashir Adamu Aliyu ne ya tabbatar da hakan jin kadan bayan kamala sanya hannu a takaddun yarjejeniyar fahintar juna tsakanin hukumar lura da kuma masu makarutu masu zaman kansu bisa kulawar ma’aikatar shari a ta jahar kano.

Da dumi-dumi: Kungiyar Kwadago ta Bayyana Ranar Fara Yajin Aiki a Nigeria

” Mun zauna da wakilan gwamnatin kusan Kwanaki 10 da suka gabata, kuma mun cimma matsaya hakan tasa muka Sanya hannu kan yarjejeniyar a wajen kotun don haka zamu janye karar da muka kai gwamnatin jihar Kano “. Inji Adamu Aliyu

Yace a matsayin su na shugabannin kungiyoyin makarantu masu zaman kansu zasu cigaba da bin ka’idojin gwamnati domin samar da ingantaccen ilimi ga al’ummar jihar kano.

Dawo da Sanusi Matsayin Sarkin Kano Ba Zai Haifawa Kano Da Mai Ido Ba – Wata Kungiya ga Majalisa

Da yake jawabi Kwamishinan sharia na jihar kano Barista Haruna Isah Dederi wanda ya samu wakilcin babban sakataren ma’aikatar Mustafa Muhammad ya bayyana yadda zaman sulhun ya kasance tare da kiran bangarorin biyu su rinka tattaunawa lokaci zuwa lokaci don Karin fahintar juna.

” Gwamnatin jihar kano bata da nufin muzgunawa masu makarantu masu zaman kansu, muna kokarine kawai don su kyautata aikin don samar da ingantaccen ilimi ga yaran a jihar kano”. A cewar Mustafa Muhammad

Yace sun sami fahimtar juna tsakanin su da Kungiyoyin, yanzu sun dinki duk wata matsala dake tsakanin, kuma nan bada jimawa zasu sanar da kotu cewa sun warware rikicin dake tsakanin su.

Tun da farko da yake jawabi mai bawa Gwamnan kano shawara kan makarantu masu zaman su a kano Comrade Baba Abubakar Umar yace hukumar bata da nufin tsaurarawa masu makarantun saidai kawai domin tabbatar da cewa ana bin doka da Gwamnatin jahar Kano samar.

Taron zaman sulhun dai ya gudana a maaikatar shariar ta jahar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...