Tsadar Kayan Abinchi: Kotu Ta Baiwa Gwamnatin tarayya Umarni

Date:

Babbar Kotun Tarayya da ke Legas ta umarci Gwamnatin Tarayya da kayyade farashin kayan masarufi da na man fetur cikin kwanaki bakwai.

Mai shari’a Ambrose Lewis-Allagoa ya ba da wannan umarni ne ranar Laraba a shari’ar da mai rajin kare hakkin bil’adama Femi Falana ya maka Jukumar Kula da Farashin Kayayyaki da kuma Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya kan tsadar rayuwa a kasar.

Ban ce Na fi Yan Najeriya Shan Wahalar Tsadar Rayuwa ba, amma ina Fatan Matsalar ta zamo Tarihi -Dangote

Alkalin ya ba wa gwamnati kwana bakwai ta kayyade farashin madara, fulawa, gishiri, sukari, kekuna, ashana, babura da motoci da kayayyakinsu da kuma man man fetur da dizal da kananzir.

Falana ya garzaya kotun ne yana neman ta umarci hukumar kayyade farashi ta gudanar da aikinta, kamar yada dokar dokar kayyade farashin kaya ta tanadar.

Da dumi-dumi: An kai Batun Rushe Masarautun Kano da Mayar da Sanusi Matsayin Sarkin Kano Gaban Majalisa

Da yake mayar da martani, Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi (SAN), ta bakin mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Kamarudeen Ogundele, ya ce, “Da zarar mun samu kwafin hukuncin, za mu yi nazari a kai.

“Za mu dauki matakin da zai dace da kasar kuma mana tabbatar muku cewa wannan gwamnati za ta kasance da muradin talakawa a koyaushe,” in ji shi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...