Gobara ta Kone Kayan Abinchi da Dabbobi a Kano

Date:

Daga Umar Ibrahim Kyarana

 

Wata gobara da ta tashi inda ta lalata kayayyakin abinci da Dabbobi da kayan sawa na dubban Nairori a garin Torankawa da ke karamar hukumar Bunkure.

Hakan na kunshe ne a cikin rahoton da aka karantawa mai martaba Sarkin Rano Ambasada Kabiru Muhammad Inuwa a yau Laraba 07/02/2024 a fadar sa.

A cewar rahoton daga Galadiman Rano Hakimin Bunkure Alhaji Muhammad Isa Umar, ya bayyana cewa gidaje bakwai masu dakuna ashirin da takwas sun kone kurmus yayin gobarar.

Da dumi-dumi: An kai Batun Rushe Masarautun Kano da Mayar da Sanusi Matsayin Sarkin Kano Gaban Majalisa

Rahoton da aka karanta ya bayyana cewa ba a samu asarar rai ba, kuma gobarar ta tashi ne daga wani wurin dafa abinci na gidan Ya’u Haladu wanda ta kai ga sauran gidajen dake makwabta da inda gobarar ta tashi.

Da yake karbar rahoton, Sarkin Rano Ambasada Kabiru Muhammad Inuwa ya girgiza matuka game da jin lamarin, kuma ya bukaci mutane musamman mata da su tabbatar da kashe wuta bayan su ne gama amfani da ita saboda gudun afkuwar hakan a nan gaba.

Ƙaranci Sadaki: Mal Ibrahim Khalil ya kalubalanci Batun Naira 100, ya fadi hakikaninsa

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in yada labaran shiyyar Rano Nasiru Habu Faragai ya aikowa kadaura24.

Sarkin, ya roki Allah Madaukakin Sarki da ya mayar wa wadanda suka yi asarar abubuwan da suka rasa, ya kuma yi addu’ar Allah ya kiyaye afkuwar irin wannan hadari.

Da aka yi hira da shi jim kadan da zama a fadar, Hakimin kauyen Torankawa Alhaji Ali Ado ya yi karin haske kan yadda lamarin ya kasance.

A wani labarin kuma a yau ne Sarkin Rano Ambasada Kabiru Muhammad Inuwa ya karbi bakuncin sabon kwamandan hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa mai kula da yankin Rano. Alhaji Ibrahim Baba Yaro wanda ya ziyarci Sarkin a fadarsa domin gabatar da kansa tare da neman albarkar Sarkin.

Sarkin, ya yi maraba da sabon Kwamandan yankin, tare da yi masa fatan yin koyi da abokin aikin sa da ya bar yankin ta hanyar zaman lafiya da mutanen yankin domin samun nasarar aikinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...