Iftila’i: Gobara ta Hallaka Wani Yaro Dan Shekara 4 a Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da mutuwar wani yaro mai kimanin shekaru hudu mai suna Abubakar Sani sakamakon gobarar da ta tashi a Yakasai Layin Inuwa mai mai karamar hukumar birnin kano .

Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Alhaji Saminu Abdullahi ya bayyana hakan a Kano.

Saminu ya bayyana cewa, hukumar ta samu kiran gaggawa daga ma’aikacinsu Habibi Adamu game da barkewar gobara a Yakasai.

Ali Nuhu Ya Ziyarci Sarkin Kano, A Karon Farko

Ya kuma yi nuni da cewa, nan take aka hada tawagar ceto daga Ofishin hukumar kashe gobara dake Sakatariyar Audu Bako a birnin Kano .

Jami’in hulda da jama’a ya yi nuni da cewa, ginin bene daya mai tsawon mita 40 da 30 da ake amfani da shi a matsayin gidan zama, daki daya dake benen ne ya kone gaba daya sakamakon gobarar, yayin da falo daya ya dan kone.

Da dumi-dumi: Shugaban Karamar Hukuma a Kano Ya Ajiye Aikinsa

Ya ce, Yaron ya makale a dakin da wuta ta kama har ta cinye shi kuma duk kokarin da aka yi na ceto shi kafin isowar ‘yan kwana-kwana ya ci tura.

Saminu ya ci gaba da cewa, an ceto wanda abin ya shafa a sume kuma aka kai shi asibitin kwararru na Murtala Muhammed, inda likitan da ke bakin aiki ya tabbatar da rasuwarsa.

Jami’in hulda da jama’a ya bayyana cewa, an mika mamacin ga mahaifinsa, Sani Hussaini domin yi masa jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Ya ce gobarar ta tashi ne sakamakon yadda yaron da abin ya shafa ke wasa da ashana a cikin daki.

Saminu ya bukaci iyaye da su daina jefa ’ya’yansu cikin hadari ta hanyar barin su ba tare da kula da su ba da kuma nisantasu da abubuwa masu hadari .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...