Ali Nuhu Ya Ziyarci Sarkin Kano, A Karon Farko

Date:

 

Shugaban Hukumar Fina-finai ta Kasa, kuma jarumi a masana’antar Kannywood, Ali Nuhu, ya kai wa Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, ziyarar ban-girma a fadarsa.

Ana iya cewa, zuwan Ali Nuhu Fadar Sarkin Kano tare da wasu fittattun ’yan Kannywood, ita ce ziyarsa ta farko ga sarakuna a fadin Najeriya tun bayan nada shi a mukamin.

Rundunar Yan sandan Kano Ta Kama Wani Kasurgumin Mai Garkuwa da Mutane

Bayan ziyarar ce, Ali Nuhu ya rubuta a shafinsa na Facebook cewa, “Godiya da jinjina ga Mai Martaba Sarkin Kano @hrh_aminu_ado_bayero CRR CNOL JP da irin adduo’i da shawarwari da aka ba mu.

“Allah Ya bamu ikon yin biyayya a matsayin mu na ’ya’ya, Ya kuma ja da ran sarki, Allah Ya rika da hannayenka, bijahi rasulillah sallalahu alaihi wa sallam.

Tsadar Abinchi: Abubuwa 3 da Gwamnan Kano Ya Fadawa Yan Kasuwa Yayin Ganawar sa Da Su

“Allah Ya sa wannan mukami ya zama alheri, Ya kuma kare mu daga duk wani sharri da ke tare da shi,” in ji shugaban hukumar fina-finan.

Kano dai ita ce cibiyar Kannywood, uwan masana’antar fina-finan Hausa a Arewacin Najeriya da ma ketare.

Masana’antar wadda daga cikinta Ali Nuhu ya fito, ya kuma samu daukaka na fatan shugabancinsa a hukumar zai ba ta damar samun ci gaba da kuma karin shiga a wajen gwamnati ta yadda za a rika damawa da ita yadda ya kamata.

Masana’antar Kannywood dai ta taka muhimmiyar rawa ta hannun mawaka da sauran jarumanta a lokacin yakin neman zabe, inda kuma suke fata ba za su tura mota ta tafi ta bar su da kura ba.

Daily Trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...