INEC ta Bayyana Sakamakon Yan Majalisun Jihar Kano Guda biyu

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana dan takarar jam’iyyar NNPP , Alhassan Ishaq, a matsayin wanda ya lashe zaben da aka yi ranar Asabar a mazabar Kura/Garun Mallam a jihar Kano.

Baturen zaben na INEC Farfesa Shehu Galadanchi ya bayyana cewa Ishaq na jam’iyyar NNPP ya samu kuri’u 37,262 inda ya doke Hayatu Musa Daurawa sallau na jam’iyyar APC, wanda ya samu kuri’u 30,803.

Yanzu-yanzu INEC ta Bayyana Dalilan ta na Dkatar da Zaɓen Kunchin da tsanyawa

Idan dai za a iya tunawa kotun daukaka kara ce ta umarci INEC da ta sake gudanar da zabe a rumfuna 20 na mazabar Kura/Garun Malam a jihar Kano.

Haka kuma, INEC ta ayyana Bello Butu-Butu na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben da aka yi ranar Asabar a mazabar Rimin Gado/Tofa.

Babban Baturen zaben Farfesa Ibrahim Tajo Suraj ya sanar da cewa Bello Butu-Butu na jam’iyyar NNPP ya samu kuri’u 31,135 inda ya doke abokin takararsa na APC wanda ya samu kuri’u 25,577.

Kotun daukaka kara ta kuma umurci INEC da ta sake gudanar da zabe a rumfunan zabe 33 a mazabar Rimin Gado/Tofa dake jihar kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

A Gaggauce: Fadar shugaban Kasa ta musanta murabus din Sakataren gwamnatin tarayya

Daga Rahama Umar Kwaru Fadar shugaban Kasa ta musanta labarin...

Gawuna ya mika ta’aziyyar rasuwar Alhaji Aminu Dantata

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano Dr. Nasiru Yusuf Gawuna...

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...