Gobara ta kone ofisoshi 17 a sakatariyar wata karamar hukumar a Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tabbatar da afkuwar gobarar da ta tashi a safiyar Larabar nan, wadda da ta kone ofisoshi 17 a sakatariyar karamar hukumar Gwale.

Abdullahi ya ce lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Laraba.

“Mun samu kiran waya da misalin karfe 03:43 na safe daga Abdullahi Hassan cewa gobara ta tashi a sakatariyar Gwale.

Talla

Kadaura24 ta rawaito Jami’in hulda da jama’a na hukumar Alhaji Saminu Abdullahi ya tabbatarwa kamfanin dillancin labarai na kasa NAN a Kano.

“Bayan samun labarin, mun aika da motar kashe gobara zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 03:46 na safe domin shawo kan gobarar,” inji shi.

Hayaniya Ta Kaure A Majalisar Kano Kan Kudaden Masarautu

Abdullahi ya ce benen da aka yi amfani da shi a matsayin ofis mai tsawon kafa 300 x 200 da sauransu, wanda ya kai 17, ya lalace gaba daya.

Ya kuma ce an kona motar motar kirar Peugeot 406, motar Haice guda daya da motar daukar marasa lafiya ta tasha.

Ya ce hukumar na binciken musabbabin tashin gobarar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...