NNPP ba ta tattaunawa da kowacce jam’iyyar don yin hadaka – ‘Yan Majalisar NNPP

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

Gamayyar yan majalisun tarayya na jam’iyyar NNPP sun ce babu wata tattaunawa da jam’iyyarsu take yi da wata jam’iyyar domin hadawa a Nigeria.

“An jawo hankalinmu a kan wani labari da wasu kafafen yaɗa labarai ke watsawa cewa jam’iyyarmu ta NNPP ta fara tattaunawa da PDP da ma wasu jam’iyyun don yiwuwar haɗewa da su”.

Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Hon. Abdulmumini Jibril Kofa ya sanyawa hannu a madadin sauran yan majalisun, wadda aka aikowa kadaura24.

Hukuncin Kotun Koli: ‘Yan sanda sun yi sabon gargadi ga al’ummar jihar Kano

“Sam babu ƙamshin gaskiya a wannan labarin, ƙarya ce tsagwaronta. Matsayin NNPP ba ɓoyayye ba ne a kan batun yin alaƙa da wasu jam’iyyu, inda muka ce a shirye muke mu yi aiki tare, mu yi ƙawance ko ma haɗaka da APC, PDP, LP ko ma kowacce jam’iyya”. A cewar Kofa

“Amma a halin yanzu babu wata tattaunawa da muke yi da kowacce jam’iyya kuma ba mu halarci kowanne irin taro don tattauna yiwuwar yin haɗaka da PDP ko ma kowacce jam’iyya ba. Wannan aikin masu neman tayar da zaune tsaye ne kuma abin da suke ƙoƙarin yi ke nan”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...