Da dumi-dumi: Gwamnan Kano Abba Kabir ya nada wanda zai kula da ofishin sakataren gwamnatin jihar

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya umurci shugaban ma’aikatan Abdullahi Musa da ya kula da ofishin sakataren gwamnatin jihar Kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar yau a Kano.

Talla

Nadin ya biyo bayan hutun jinya da SSG Dr. Abdullahi Baffa Bichi ya tafi kasar Saudiyya domin neman lafiya.

Dalilin da yasa kotu ta bada umarnin rufe asusun gwamnatin Kano

A wata takarda mai dauke da sa hannun shugaban ma’aikatan fadar gwamna Hon. Shehu Wada Sagagi, Shugaban Ma’aikata zai cigaba da kula da ofishin sakataren gwamnatin har sai Dr. Baffa Bichi ya dawo nan da ‘yan makonni masu zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...