Sake baiwa Aminu Dahiru mukami, Ganduje ya ajiye kwarya a gurbinta – Baban Nura

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

 

Jarumin nan na masana’antar Kannywood Rabi’u Musa wanda aka fi sani da baban Nura ya yabawa Shugaban jam’iyyar APC na Ƙasa Dr Abdullahi Umar Ganduje bisa sake nada Aminu Dahiru a matsayin babban mataimakinsa na musamman kan harkokin daukar hoto mai motsi da taruka .

” Babu shakka Aminu Dahiru jajirtaccen matashi ne da baya wasa da aikinsa kuma yake da gaskiya da rikon amana da ya cancanci rike kowanne irin mukami”.

Rabi’u Musa Baban Nura ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da jaridar kadaura24.

Talla

Yace yana da yaƙinin Aminu Dahiru ba zai taba baiwa shugaban jam’iyyar APC na Ƙasa Kunya ba, saboda kokarin su wajen sauke duk wani nauyi da aka dora masa.

Gwamnatin tarraya ta bayyana dalilan da yasa wasu ma’aikatanta basu sami albashin watan Nuwamba ba

“Ina amfani da wannan dama wajen taya Aminu Dahiru murnar samun wannan Muƙami, tare da fatan Allah ya bashi damar sauke nauyin da Ganduje ya dora masa kamar yadda ya sauke a baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...