Dalilin da yasa kotu ta bada umarnin rufe asusun gwamnatin Kano

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta bayar da umarnin dakatar da wasu daga cikin asusun gwamnatin jihar Kano a wasu bankunan kasuwanci guda 20 a Najeriya.

Mai shari’a I.E Ekwo ya bayar da wannan umarni ne a wata kara da masu shaguna a filin idi da kungiyar ‘yan kasuwa suka shigar a kan ruguza shagunansu da gwamnatin Kano tayi, wanda suka bayyana a matsayin haramtaccen matakin da gwamnati ta dauka a watan Yunin 2023.

Talla

Kadaura24 ta ruwaito cewa wadanda suka shigar da karar, Alhaji Awalu sai’du, Ifeanyi Nwobodo, Alhaji Sani Uba, Alhaji Abdullahi A. Idris, da wasu mutane 25 sun kai karar gwamnatin jihar Kano, a matsayin masu bin bashi, har naira biliyan 30.

Rayukan mutanen da aka kashe a taron Maulidi ya kamata lauyoyi su bi kadi ba dimokuradiyya ba – Isa Bello ja

Umarnin yana kunshe ne a cikin daftarin hukuncin da aka bayar a ranar 28 ga Nuwamba, 2023 kuma aka bai wa manema labarai ranar Larabar nan.

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito babbar kotun tarayya dake Kano ta umarci gwamnatin jihar kano da ta biya diyyar Naira Biliyan 30 ga masu shagunan da aka rushe musu a filin idi ba bisa ƙa’ida ba.

Karin bayani na nan tafe…

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...