Tinubu ya ba da umarnin yin bincike kan harin bom a Kaduna

Date:

Daga Hafsat Yusuf Sulaiman

 

Shugaban Najeriya, Bola Ahmad Tinubu ya ba da umarnin a gudanar da cikakken bincike kan harin bom da rundunar sojin ƙasar ta ce ta kai bisa ‘kuskure’ a jihar Kaduna.

Shugaban ya bayyana haka ne yayin miƙa saƙon ta’aziyya ga al’ummar jihar Kaduna da kuma alhini ga mutanen da suka ji rauni sakamakon lamarin da ya faru a ƙauyen Tudun Biri a ƙaramar hukumar Igabi.

Talla

Cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan kafafen yaɗa labarai, Ajuri Ngelale ya fitar, Shugaban Najeriyar ya ce abin takaici ne inda kuma ya bayyana jimami kan asarar rayukan da aka yi.

Gwamnatin tarraya ta bayyana dalilan da yasa wasu ma’aikatanta basu sami albashin watan Nuwamba ba

Shugaban Najeriyar ya kuma buƙaci mutane su kwantar da hankalinsu yayin da hukumomi ke nazari a kan lamarin.

Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin a bai wa mutanen da suka jikkata kulawa sosai a asibiti tare da addu’ar Allah ya ji ƙan waɗanda suka rasu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...