Gwamnatin tarraya ta bayyana dalilan da yasa wasu ma’aikatanta basu sami albashin watan Nuwamba ba

Date:

Daga Tijjani Mu’azu Aujara

 

Gwamnatin Najeriya ta ce har yanzu ma’aikatan wasu hukumomin gwamnatin tarayya ba su samu albashin su na watan Nuwamba ba ne, saboda hukumomin sun karar da kasonsu na kasafin kuɗin wannan Shekarar mai karewa.

Kadaura24 ta rawaito Ministan harkokin kudi, Wale Edu ne ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da manema labaran fadar shugaban kasa a Abuja.

Wasu hukumomi irin su manyan makarantun tarayya da FRCN, ba su biya ma’aikatansu albashin watan Nuwamba ba.

Talla

“Duk hukumomin da abin ya shafa sun gama kashe kudadensu na kasafin kudi kuma an rufe tsarin da yake Basu damar biyan albashin,” in ji shi

Mista Wale Edu, ya ce gibin na kunshe ne a cikin kasafin da majalisar ta amince da shi kwanan nan.

Yadda Jirgin Sojin Nigeria ya yi ruwan bam a kan masu taron Mauludi a Kaduna

Ya ce ma’aikatarsa ​​”kawai ta sami shawarwari game da gibin a ranar Litinin” kuma ana kokarin ganin an dawo da hukumomin kan tsarin da ya dace domin su sami damar biyan kudaden ma’aikatan na su .

Da yake karin haske kan dalilin da ya sa hukumomin suka karar da kudaden, Mista Wale Edun ya ce wasu hukumomin sun dauki karin ma’aikata ba tare da sanar da ma’aikatar kudi akan lokaci ba.

“Ya kamata hukumomin su gaya mana akan lokaci domin a dauki matakan da suka dace,” in ji ta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...