Dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji Hon. Abdulmumini Jibril Kofa ya sauke kabakin arziki na Naira Miliyan 20, ga wasu shugabanni 513 daga sassa daban-daban a yankinsa .
“Wannan ba shi ba ne karon farko da muka ba da irin wannan tallafi ga wadannan shugabannin na mu, kuma ba zai zama na ƙarshe ba, zamu cigaba da tallafa muku don baku damar sharbar rokon Dimokaradiyya”. Inji shi
Kadaura24 ta rawaito Hon. Abdulmumini Kofa ya bayyana hakan ne lokacin da raba kudin ga shugabannin sassan a ranar lahadi.

Yace a makwanin biyu da suka gabata ya bayar da tallafi ga kungiyoyin dalibai da sauransu, yanzu Kuma yace wadanda zasu amfana da tallafin na wannan karon sune shugabannin jam’iyyar NNPP na kananan hukumomin Kiru da Bebeji da na mazabu da kungiyoyin limamai da na mafarauta da dai sauransu.
Yadda Jirgin Sojin Nigeria ya yi ruwan bam a kan masu taron Mauludi a Kaduna
” Ina so ku sani indai batun aiki ne da kuma bada tallafin ragewa al’umma radadin halin da ake ciki ne, to Ina baku tabbacin ku je gida ku yi bacci har da minshari domin yanzu na fara kuma zan yi tayi har sai kunce ya isheku”. Inji Kofa
Dan majalisar ya kuma godewa al’ummar Kananan hukumomin Kiru da Bebeji da bebeji bisa hadin kai da suke bashi har ya fara samun damar cika wasu daga cikin alkawuran da yayi musu yayin yaƙin neman zaɓe.