Dan majalisar Kiru da Bebeji ya ba da tallafin Naira Miliyan 20 ga wasu kungiyoyin yakin

Date:

 

Dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji Hon. Abdulmumini Jibril Kofa ya sauke kabakin arziki na Naira Miliyan 20, ga wasu shugabanni 513 daga sassa daban-daban a yankinsa .

“Wannan ba shi ba ne karon farko da muka ba da irin wannan tallafi ga wadannan shugabannin na mu, kuma ba zai zama na ƙarshe ba, zamu cigaba da tallafa muku don baku damar sharbar rokon Dimokaradiyya”. Inji shi

Kadaura24 ta rawaito Hon. Abdulmumini Kofa ya bayyana hakan ne lokacin da raba kudin ga shugabannin sassan a ranar lahadi.

Talla

Yace a makwanin biyu da suka gabata ya bayar da tallafi ga kungiyoyin dalibai da sauransu, yanzu Kuma yace wadanda zasu amfana da tallafin na wannan karon sune shugabannin jam’iyyar NNPP na kananan hukumomin Kiru da Bebeji da na mazabu da kungiyoyin limamai da na mafarauta da dai sauransu.

Yadda Jirgin Sojin Nigeria ya yi ruwan bam a kan masu taron Mauludi a Kaduna

” Ina so ku sani indai batun aiki ne da kuma bada tallafin ragewa al’umma radadin halin da ake ciki ne, to Ina baku tabbacin ku je gida ku yi bacci har da minshari domin yanzu na fara kuma zan yi tayi har sai kunce ya isheku”. Inji Kofa

Dan majalisar ya kuma godewa al’ummar Kananan hukumomin Kiru da Bebeji da bebeji bisa hadin kai da suke bashi har ya fara samun damar cika wasu daga cikin alkawuran da yayi musu yayin yaƙin neman zaɓe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...