Hukumar kula da Shari’a a Nigeria ta magantu kan rudani game da hukuncin kotun daukaka kara na kujerar gwamnan Kano 

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim
 Hukumar dake kula da shari’a ta kasa (NJC) ta sha alwashin hukunta jami’an shari’a da suke da alhaki wajen haifar da rudani game da  hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke kan rikicin zaben gwamnan Kano.
 Hukumar ta bayyana hakan ne yayin wata ziyarar ban girma da jami’an NJC suka kai hedkwatar kamfanin Media Trust Limited da ke Abuja ranar Talata, kamar yadda Daily trust ta ruwaito.
 Kadaura24 ta tuna cewa kotun daukaka kara da ke Abuja a ranar 17 ga Nuwamba, 2023 ta soke zaben gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP tare da bayyana abokin hamayyarsa Nasiru Gawuna na jam’iyyar adawa ta APC nasara a matsayin gwamnan jihar kano.
Talla
 Amma a cikin takardar kundin bayanan hukuncin kotun da aka fitar kwanaki hudu bayan yanke hukuncin, kotun daukaka kara a rubuce ta canja bayaninta tare da bayyana Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben a karshen takardar.
 Sai dai jami’an hukumar Shari’ar sun ce sun samu koke da yawa kan lamarin inda suka yi alkawarin yin nazari tare da ɗaukar matakin da ya dake ga wadanda aka samu da laifin haddasa rudani kan hukuncin na kano.
 “Ba za a yi gaggawar yarda da koke-koken ba, sai an tantance korafe-korafe da farko, wadanda za su duba, sai su aika zuwa zauren majalisa, sai majalisar ta duba ta kuma kafa kwamiti. Za a kirawo alkali da masu shigar da koken domin bin diddigi,” shugaban tawagar ya shaida wa jaridar.
 Jami’in na NJC ya ce hukumar da ke kula da shari’a za ta binciki cece-kucen da ake yi duk da cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya hada da CTC da suka saba wa hukuncin kotun daukaka kara a matsayin batun daukaka kara a kotun koli.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta magantu kan Hukuncin kotu na zaben kananan hukumomi

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Kano ta bayyana farin...

Kotun daukaka kara ta yanke hukunci kan zaben kananan hukumomin Kano

Kotun ɗaukaka kara dake Abuja, ta rushe hukuncin babbar...

Dole ne yan Nigeria su dage da yawaita addu’o’i a kwanaki 10 Zulhijja – Sheikh Muhd Nasir

Daga Usman Hamza Shugaban majalisar limaman masallatan juma'a na Nigeria...

Mun kama mutanen da mu ke zargi da kashe DPO Rano – Kiyawa

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta...