Yadda Wani Kwale-kwale ya Kama da Wuta Yana tsaka da Tafiya a Ruwa a Jihar Neja

Date:

Daga Abubakar Mustapha

Rahotanni daga jihar Neja na cewa wasu mutane uku sun bace bayan da wani jirgin fasinja na katako ya kone kurmus, jim kadan bayan tashinsa a unguwar Katcha da ke karamar hukumar Katcha a jihar Neja a ranar Juma’a.

A cewar wani ganau, Abdulmalik Adamu, lamarin ya faru ne da misalin karfe 6 na yamma jim kadan bayan kwale-kwalen ya kammala lodin kaya da fasinjojin da zasu koma garuruwansu bayan kammala cin kasuwar Katcha wadda take ci mako-mako.

Talla

Ya ce matukin kwale-kwalen yana tsaka fa sarrafa injin ne sai kwale-kwalen ya kama da wuta, lamarin da ya tilasta wa fasinjoji yin tururuwar fita daga jirgin domin tsira da rayukansu.

Shirin Dadin-Kowa ya sa samari son yin wuf da ni – Fati Harka

Da yake tabbatar da faruwar lamarin ga gidan Talabijin na Channels, shugaban masu gudanar da sanar kwale-kwalen na Katcha, Dangana Mai kwale-kwale, ya tabbatar da batan mutane uku wadanda yace duk Yara ne , amma bai bayyana musabbabin tashin gobarar ba, sai dai ya ce jirgin ya kone kurmus tare da wasu kayayyaki na miliyoyin naira.

Wasu masunta daga gudanar da harkokin su a wajen sun taimaka wajen kwaso wasu daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da su tare da gaggauta nesanta jirgin da ke konewa da wasu .

Talla

Jirgin ruwan dai ya ɗauki fasinjoji ne zuwa garuruwan Zakanti, Danbo da wasu yankuna dake gabar ruwan wadanda suke cikin kananan hukumomin Katcha da Agaie a jihar Neja.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Tsohon ɗan majalisar tarayya, Farouk Lawan, ya bayyana cewa...

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...