Kungiyar PACF ta zabi Dr. Abubakar Tanko a matsayin Sakatare Janar

Date:

Daga Maryam Muhammad Ibrahim

 

Kungiyar bunkasa gasa ta kasa da kasa ta Africa mai suna Pan African Competitiveness Forum ta zabi Dr. Abubakar Tanko Bala hamshakin kasuwar nan a matsayin Sakatare janar kungiyar reshen Nigeria .

 

Dr. Abubakar Tanko Bala hamshakin dan kasuwa ne kuma mashawarci kan harkokin kasuwanci, haka zalika shi ne Ma’ajin Kungiyar Kananan Masana’antu ta Nigeria (NASSI).

Talla

A wata sanarwa da Kakakin ofishin babban Sakataren dake Nigeria Fa’iza Shehu ta aikowa kadaura24, tace a ranar Juma’a 1 ga watan Satumbar, shekara ta 2023, Dr. Abubakar Tanko ya zama babban sakataren kungiyar Pan African Competitiveness Forum (PACF) wanda aka gudanar da bikin a Sheraton Hotel Abuja.

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya Nada Karin Manyan Mataimaka 57

Ita dai kungiyar Pan African Competitiveness Forum wato PACF an ƙirƙire ta ne don haɓaka tattalin arziƙin ƙasashen Afirka ta hanyar samar da Ƙungiyoyin da za su inganta tare da haɓaka tsakanin waɗannan ƙasashe.

Alh Garba Ibrahim Gusau Mni, MFR, wanda kuma shi ne shugaban kungiyar PACF tare da ma’ajin kungiyar na kasa Alhaji Abdul-Fatah Shittu sune suka jagoranci taron tare da rantsar da Dr. Abubakar Tanko Bala matsayin babban sakatare na kungiyar PACF.

Bikin wanda aka yi shi cikin nasara da kyakyawan fatan Dr. Abubakar zai taka muhimmiyar rawa wajen ciyar da kungiyar PACF gaba a matsayinsa na Sakatare Janar sakamakon ya cancanci rike mukamin da aka zabe shi.

Kungiyar Pan African Competitiveness Forum dai ta na da karfi Sosai tana bada gudunmawa matuka wajen cigaban tattalin arzikin kasashen Africa, sanna kuma tana cikin kungiyar kasashen Africa wata AU, tana Kuma da alaka da kungiyoyin taimakawa al’umma na kasashen duniya sama da 72.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...