Kungiyar Kasuwar Kwari ta zabi sabbin shuwagabanni

Date:

Daga Khadija Aliyu

 

Kungiyar ‘yan kasuwar Kantin kwari ɓangaren yan tebura dake jihar kano ta zabi sabbin shugabannin da za su jagorance ta na tsawon shekaru hudu masu zuwa.

 

Zaben wanda ya gudana a Kano, ya samu halartar dimbin ‘yan kasuwa, da wakilai daga kungiyoyi daban-daban, da masu ruwa da tsaki na kasuwar.

Talla

Wadanda aka zaba sun hada da, Alhaji Ishaq Alkasim Tatari chairman, mataimakin Shugaban I, Alhaji Ali Isah Musa, mataimakin Shugaban II Alhaji Manniru Yunusa Dandago, Sakatare janar Alhaji Musa Umar Sanda, sai Alhaji Akilu Salihu a matsayin mataimakin Sakatare.

Emefiele: DSS ta kama mataimakin gwamnan CBN Kingsley Obiora

Sauran sun hada da, Alhaji Yakubu Baita sakataren kudi, mataimakin sakataren kudi Alhaji Abdulhamid, ma’aji Alhaji Musa Tijjani Thaiba, Mai bincike I da na II, Alhaji Sammmani El- Samad da Alhaji Hassan Muhammad.

Kungiyar kwadago NLC ta sanar da ranar da zata tsunduma yajin aikin gargaɗi

Barista Kabiru Isah Jibril zai kasance mai ba da shawara kan harkokin shari’a, yayin da Alhaji Saifullahi Lawan Ahmed, da Alhaji Usman Sulaiman suka zama PRO I & II.

An zabi jami’in jin walwalar yan kungiyar I & II, da sakatare tsare-tsare , kuma jami’in kasashen waje I & II, sun haɗar da Alhaji Kabiru Ya’u, Alhaji Salisu Adamu Kura, Alhaji Baffa A.Baffa, Alhaji Abubakar Babayo da Alhaji Rabi’u Musa Kabara.

 

Dattawan kungiyar 6 sun hada da: Alhaji Jamilu Ata, Alhaji Lawan Safiyanu, Alhaji Hassan Muhammad, Malam Mustapha, Alhaji Sulaiman Saleh, Alhaji Abubakar Abdurrahman, yayin da Alhaji Kabiru Sarki Sagagi da Alhaji Auwalu Abdullahi.

Da yake jawabi jim kadan bayan rantsar da su a matsayin sabbin shugabannin kungiyar, shugaban kungiyar ‘yan kasuwar Kantin Kwari, Alhaji Ishaq Alkasim Tatari ya yi alkawarin yin aiki kamar yadda kundin tsarin mulki kungiyar ya tanada, domin kare muradun ‘yan kasuwar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...