Emefiele: DSS ta kama mataimakin gwamnan CBN Kingsley Obiora

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

 

Hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta kama mataimakin gwamnan babban bankin Najeriya mai kula da manufofin tattalin arziki Kingsley Obiora.

 

Wani rahoto da jaridar Peoples Gazette ta fitar ta ce, yanzu Mista Obiora ya shafe kwana hudu a hannun DSS, inda hukumar take yi masa tambayoyi, inda ta ke duba zargin karkatar da kudi a karkashin Godwin Emefiele, hambararren gwamnan babban bankin.

Talla

Mista Emefiele, wanda aka fara nada shi gwamnan CBN a watan Yunin 2014, ya kasance a hannun DSS tun ranar 10 ga watan Yunin 2023, kwana guda bayan da shugaba Bola Tinubu ya tsige shi daga mukaminsa.

An yi Garkuwa da Matan Yan Bindiga a Zamfara

Yayin da wasu alkalan Kotunan tarayya biyu ne suka bayar da umarnin a saki Mista Emefiele, amma hukumar DSS na ci gaba da samun wasu dalilai na tsare shi , inda sukan shigar da sabbin tuhume-tuhume domin maye gurbin wadanda aka fara gurfanarwa a gaban kotu.

Wata majiya mai tushe ta ce an kama Mista Obiora ne a matsayin babban shaida kan maigidan sa Emefiele.

Kungiyar kwadago NLC ta sanar da ranar da zata tsunduma yajin aikin gargaɗi

Mista Obiora, wanda aka haifa ranar 6 ga Maris, 1976, ya kasance babban jami’in tsare-tsare a asusun lamuni na duniya, ya kuma shawarci tsohuwar ministar kudi Ngozi Okonjo-Iweala. Ya kuma kasance mai ba Mista Emefiele shawara har zuwa ranar 2 ga Maris, 2020, lokacin da aka tabbatar da shi a matsayinsa na daya daga cikin mataimakan gwamnoni hudu na CBN.

Mista Tinubu, a karshen watan Yuli, ya nada wani Kwamitin bincike na musamman da zai binciki CBN da sauran hukumomin tarayya da ake zargin sun da satar jama’a. Jim Osayande Obazee ya koma bakin aiki a farkon watan Agusta a babban bankin kasar CBN, in ji jami’ai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Ganduje ya yi murabus daga shugaban jam’iyyar APC na kasa

Daga Abdullahi Shu Shugaban jam'iyyar APC na kasa Abdullahi Umar...

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...