Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta ce ta sayo kayan daki da sauran kiyayyakin ma’aurata 1,800 a karkashin shirinta na aurar da zawarawa .
Babban kwamandan hukumar Sheikh Aminu Daurawa ya bayyana haka a lokacin da ya duba wasu kayayyakin auren a ranar Laraba a Kano.

Ya ce gwamnati ta ware sama da Naira miliyan 800 don siyan kayan sawa, kayan abinci, kayan daki, da sauran kayayyakin bukatu na bikin aure.
“Kowace Amarya za ta samu katifa, matashin kai, da kuma Naira 20,000 domin fara sana’a.
Yanzu-Yanzu: NNPP ta dakatar da Kwankwaso
“Wasu masu hannu da shuni sun yi alkawarin bayar da gudummawar kason su don ganin an samu nasarar gudanar da auren zawarawar.
“Ma’aurata 1,800 za su amfana da wannan shirin, wanda zai taimaka matuka wajen dakile munanan dabi’u da talauci a tsakanin al’umma, saboda akan dage aure da yawa, saboda rashin abun da iyaye zasu aurar da ‘ya’yansu ,” inji shi.
Daurawa ya ce za a sanar da ranar daurin auren ne domin baiwa mazauna yankin da masu sha’awar bayar da gudumawar kason su domin cimma nasarar da ake da bukata.
Ya kara da cewa an gindaya sharudda na zabar wadanda za su ci gajiyar shirin, ya kara da cewa wadanda suka saki matansu ba da wani dalili mai kwari ba, sai sun biya gwamnati kudin da ta kashe musu.