Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa
Kotun daukaka kara, dake babban birnin tarayya Abuja ta kori karar da Abba Kabir Yusuf ya shigar na neman a yi watsi da hukuncin kotun Sauraren kararrakin zaben karkashin jagorancin mai shari’a Oluyemi Akintan Osadebay da ta zartar a ranar 13 ga Yuli, 2023.

Majiyar Kadaura24 ta Justice watch ta rawaito cewa a hukuncin da ta yanke a yau Alhamis, Kotun ta bayyana karar da Abba K. Yusuf ya shigar a kan APC da wasu mutane 2 a matsayin “marasa tushe, wadda da kuma ta cancanci hukuncin kora”.
Ƙarin bayani na nan tafe….