Gwamnan Kano ya bamu umarnin cigaba da aikin tituna masu tsahon kilomita 5 a wasu kananan hukumomi – Kwamishinan aiyuka

Date:

Daga Aisha Sani Bala

Gwammantin jihar Kano tace zata ci gaba da wasu ayyukan tituna masu kilo mita 5 da aikin su ya tsaya a wasu kananan hukumomin a fadin jihar.

Kwamishinan ma’aikatar Ayyuka da gidaje ta jihar Injiniya Marwan Ahmad ne ya bayyana hakan, yayin da ya jagoranci ziyarta wasu daga cikin kananan hukumomi da aka ci gaba da ayyukan.

Talla

Injiniya Marwan Ahmad ya kuma ce ma’aikatar sa a shirye ya take tsaf domin ganin ta kammala aikin titinan a cikin kankanin lokaci.

 

Shugaban Mulkin Soji na Nijar ya bayyana lokacin da zasu mika Mulki ga farar hula

” Zamu tura ma’aikata dukkanin kananan hukumomin da ba’a karasa aikin titinansu masu tsahon kilomita 5 ba, domin yin aiki tukuru don kammalawa cikin lokaci kamar yadda gwamna ya bamu umarni”. Inji Kwamishinan

Wasu daga cikin al’umma yankin Gezawa da Albasu da kwamishinan ya ziyarta sun bayyanawa koken su kan matsalolin da lalacewar titunan ke haifar mu su musamman a wannn lokacin na damuna.

A baya dai Gwamnan jihar Kano injinya Abba Kabir Yusuf ya zabi wasu kananan hukumomi guda biyar domin ci gaba da ayyukan titunan masu kilo mita 5

Wakiliyar mu Aisha Sani Bala ta rawaito cewa Injiniya Marwan Ahmad ya ziyarci aikin kananan hukumomin Gezawa da Albasu ya Kuma ji koken mazauna yankin tare da yi musu alkwarin kammala aiyukan Titunan da wuri domin gujewa ambaliyar ruwan da ke haifar musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...