Yanzu-Yanzu: El-Rufai ya bayyana dalilin da yasa ya hakura da cikin cikin ministocin Tinubu

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir Ahmad El-Rufai ya janye sha’awar sa na kasancewa ciki ministoci kuma dan majalisar zartarwar gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

 

Wasu majiyoyin daga fadar shugaban kasa sun bayyana mana cewa El-rufa’i ya shaidawa Tinubu a wata ganawa da suka yi a ranar talata cewa ba ya sha’awar zama minista, amma zai ci gaba da ba da gudummawar sa domin ci gaban Najeriya a matsayinsa na dan kasa.

Talla

Ya kuma shaida wa Tinubu cewa yana bukatar lokaci don mayar da hankali kan kan Karatunsa na samun digirin digir gir a wata jami’a dake kasar Netherlands.”

Rikicin Aure: Ya kamata Hukumar Hisba ta shiga tsakanin G-Fresh da Sadiya Haruna – Auwal Danlarabawa

Majiyar ta shaida wa yan jarida cewa tsohon gwamnan ya ba da shawarar a nada wani makusancin sa a matsayin minista domin maye gurbinsa, mai suna Jafaru Ibrahim Sani, yana mai cewa zai cigaba cigaba da goyon bayan gwamnatin shugaban kasar don ciyar da ƙasar gaba .

Yanzu-Yanzu: Kotu ta Soke Zaɓen Wani Dan Majalisar Tarayya a Kano

Sani ya taba zama kwamishina a ma’aikatu uku a jihar Kaduna (ilimi da muhalli na kananan hukumomi) yayin da El-Rufai ke gwamna.

Tun bayan ya dawo Najeriya daga Landan, El-Rufai ya nemi ganawa da shugaban kasa, a wannan lokaci ya samu labarin kin tabbatar da shi da majalisar dattawa ta yi.

A ganawarsu, Shugaban kasa Tinubu ya sanar da El-Rufai cewa ya samu korafe-korafe akan sa masu yawan gaske, da yana bukatar rana daya domin ya duba su da kyau sannan ya san wani mataki zai dauka akan su.

A daidai wannan lokaci ne El-Rufai ya shaida wa Tinubu cewa, ya hakura da kujerar ministan, tunda karara na ji a jikina akwai wasu da suka zagaye shugaban Kasa da basa so na zama cikin ministocin sa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...