Daga Maryam Muhammad Ibrahim
Shugaban gidauniyar tallafawa mabukata tun daga tushe wato Grassroot Care anda Aid Foundation Amb. Auwal Muhammad Danlarabawa ya yi kira ga Hukumar Hisba ta jihar kano da ta gayyaci Sadiya Haruna da G Fresh Al’amin akan abubuwan da suke yi na wulakanta aure a sohiyal media dan kare martabar aure a Addini da al’ummar musulmi .
“Babu shakka idan hukumar Hisbah ta shiga wannan lamari za’a iya samun masalaha da daidaito a auren nasu kuma hakan zai kawo ƙarshen zubar da kimar Musulmi da Hausawa da ma’auratan biyu suke yi”.

Danlarabawa ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da yayi da wakilin Kadaura24 a Kano.
Yanzu-Yanzu: Kotu ta Soke Zaɓen Wani Dan Majalisar Tarayya a Kano
Ya Koka matuka kan irin kalamai na zubar da kima da ma’auratan suke yi a shafukansu na dandalin sada zumunta, wanda hakan bai dace ba, dukkuwa da cewa basu jima da yin aurenba.
” A koyarwar addinin musulunci da dabi’un Malam Bashaushe abubuwan da suke yi ba daidai ba ne, don haka nake kira ga Hukumar Hisba data gayyaci Sadiya Haruna da Mijinta G-Fresh Al-ameen don daidaita su ko kuma yin abun da ya dace game da auren nasu”. Inji Auwal Danlarabawa
Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa a kwanakin baya ne dai aka daura auren G-Fresh da Sadiya Haruna Kuma makonni kadan bayan auren sa’insa ta barke tsakanin su a shafukan sada zumunta.