Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Kano zata Sauyawa Yan KAROTA Kaki

Date:

Daga Zainab Kabir Kundila

 

Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamnan Alhaji Abba Kabir Yusuf ta dauki aniyar chanjawa jami’an hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Jihar kano KAROTA Kakinsu.

 

Shugaban Hukumar ta KAROTA Engr Faisal Mahmud Kabir, ne ya bayyana hakan a lokacin da jami’an hukumar na wucin gadi Marshal suka ziyarci a ofishinsa.

Talla

Yace za’a sauya musu kalar kayan da duk suke sanyawa a kokarin hukumar na Kara zaburar da ma’aikatanta don inganta aiyukan su a kano.

Da dumi-dumi: Ganduje ya baiwa tsohon kwamishinansa mukami

” Zamu yi duk mai yiyuwa wajen ganin mun Kara ingantawa da tsaftace aikin mu, Saboda jami’anmu su sami damar magance matsalolin da ake samu daga masu amfani da hanyoyi a fadin jihar kano”. Inji Engr. Faisal

Sai dai bai bayyana kalar da kakin na karotar zai koma ba, kamar yadda sanarwar da kakakin hukumar Nabulusi Abubakar Kofar Na’isa ya fitar.

Idan za’a iya tunawa a baya dai an jima an ta rade-radin gwamnatin jihar kano zata sauya yan karotar kakaki saboda wasu dalilai masu nasa ba da Siyasa

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...