Shugaban Majalisar Dattawan Nigeria ya yi subul da baka an wasu kudade

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaban Majalisar Datawan Najeriya, Godswill Akpabio ya yi suɓul-da-baka, inda ya sanar da cewa majalisar ta tura wa mambobinta ‘kuɗin more hutu’.

 

A lokacin zaman majalisar na ƙarshe kafin tafiya hutu, Akpabio ya ce “Da zarar an rantsar da Sanata Umahi a matsayin minista, za mu sake tsara shugabancin majalisar.”

Talla

Sai ya ce “Domin more hutunmu, Akawun majalisa ya tura ɗan wani abu a asusun ajiyar kowannenmu.”

Bayan ya yi furucin ne ɗaya daga cikin ƴan majalisar ya matsa kusa da shi, don fargar da shi cewa ana nuna zaman nasu kai-tsaye ta talabijin.

Da dumi-dumi: Ganduje ya baiwa tsohon kwamishinansa mukami

Daga nan ne sai Akpabio ya yi saurin warware maganar tasa, inda ya ce “Na janye kalaman da na yi. Ina nufin shugaban majalisa ya tura maku addu’ar fatan shan hutu lafiya da kuma fatan yin tafiya lafiya a dawo lafiya.”

Babu dai tabbacin game da adadin abin da aka tura wa ƴan majalisar, musamman ma yadda albashinsu da kuma sauran kuɗaɗen alawus ɗinsu duk abubuwa ne da babu hakiƙanin bayani a kai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abin mamaki: Barawo ya sace Motar dake cikin ayarin motocin gidan gwamnatin Kano

Wani barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin jihar...

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...