Shugaba Tinubu ya shiga ganawa da tsohon gwamnan Kaduna Nasir El-Rufa’i da tsohon gwamnan River Nyensom Wike a Villa.
Wasu majiyoyi sun ce ganawar na daga cikin ƙoƙarin tabbatar da naɗin El-Rufa’i a matsayin minista.

Tsaffin gwamnonin dai na daga cikin waɗanda Tinubu ya aika sunayensu majalisa domin tantance su zuwa wannan muƙami.
Da dumi-dumi: Ganduje ya baiwa tsohon kwamishinansa mukami
To sai dai majalisar ta amince da naɗin Wike, amma bata amince da El-Rufa’i ba, inda wata majiya daga fadar shugaban kasa tace ganawar Tinubu da El-Rufai na da nasaba da batun kin tantancewar da Majalisa ta yi masa.