Matsalar tsaro tasa an Sanya dokar hana fita a Adamawa

Date:

Gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri ya ayyana dokar ta-ɓaci ta tsawon sa’a 24 a fadin jihar.

Cikin wani saƙon da gwamnan ya wallafa a shafinsa ta twitter, ya ce an sanya dokar ne sakamakon ƙaruwar hare-haren da ɓata-gari ke kai wa mutane da kasuwanni a faɗin jihar.

Talla

Rahotonni daga jihar sun ce wasu ɓata-gari ne suka riƙa far wa mutane da makamai a birnin Yola tare da sace musu dukiyoyi a shagunansu.

Yajin aiki: Ku tanadi kayan abinci da magunguna a gidajenbku, NLC ga ‘yan Najeriya

Gwamna Fintiri ya ce an hana zirga-zirga a jihar, sai iya mutanen da ke ayyuka na musamman, waɗanda ke ɗauke da katin shaidar aiki.

Gwamnan wanda ya yi kira ga al’ummar jihar da su yi biyayya ga dokar, ya ce tsaron lafiyar mutanen jihar shi ne babban abin da ya sanya a gaba.24

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...